Yan sanda masu amsan cin hanci sunci mutuncin mutane

Yan sanda masu amsan cin hanci sunci mutuncin mutane

- Ance masa ya nuna katin zama dan kasa, kuma ya nuna.

- Jaridar Premium Times ta ce yan sandan sun hana wadanda suka ki basu cin hanci wuce na tsawon lokaci

Yan sanda masu amsan cin hanci sunci mutuncin mutane
Yan sanda masu amsan cin hanci sunci mutuncin mutane

An kama Wasu yan sanda guda biyu masu cin mutuncin mutane a titi da sunan aiki suna amsan cin hanci hannun mutane.

Game da cewar jaridan Premium Times wadanda sukayi shaidi faruwan a ranan Alhamus,29 ga watan Disamba, yan sandan sun tsayar da wata mota mai dauke da fasinjoji, masu suna Ali Brothers, kusa da GSM village.

KU KARANTA: Kastam ta kai shinkafa sansanin IDP

Ance Daya daga cikin hafsoshin na sanye da kayan sanyi kuma dayan ya sanya kayan yan anda dauke da suna Mohammed Azeh.

An bada rahoton cewa hafsohin sunce ma direban ya bude bayan motarsa saboda suga abinda ke ciki. Direban yayi biyayya ya fito da abinda ke ciki.

Daga baya kuma aka ce masa ya nuna katin zama dan kasa ,kuma ya nuna.

Kakakin hukumar yan sanda na Abuja, Manzah Anjuguri, wabda aka kira yace za’a gudanar da bincike cikin al’amarin.

Yace: “Ku taimaka ku fada mana inda suke, sunayensu,idan kuna da su,zamu bincike su.”

Premium Times reports that the officers involved are known to delay drivers, who refuse to part with money, for several hours.

Jaridar Premium Times ta ce yan sandan sun hana wadanda suka ki basu cin hanci wuce na tsawon lokaci.

Ku kasance tare da mu@ https://www.facebook.com/naijcomhausa https://www.twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel