Yan Najeriya sun yi jimamin mutuwar wata jarumar Soja mace

Yan Najeriya sun yi jimamin mutuwar wata jarumar Soja mace

Tun bayan bayyanar labarin mutuwar wata gwarzon jarumar soja a yan kwanakin nan ne jama’a da dama daga sassan kasar nan suke jajinta ma iyalan sojan tare da tausaya musu.

Yan Najeriya sun yi jimamin mutuwar wata jarumar Soja mace
Jarumar Soja Blessing

Ita dai Blessing Ene Edache kurtun soja ce a rundunar mayakan sojan kasa na Najeriya, kuma ta gamu da ajalinta ne sakamakon zazzabin cizon sauro, hakan ya sanya wani da yayi ikirarin shine mahaifinta ya nuna damuwarsa a fili, cike da alhini.

KU KARANTA:Dogo na Daura ya gamu da dogon Soja (Hotuna)

Shima mahaifin nata, wanda soja ne mai igiya biyu, wato Laftanr Prince C Okafor ya ce “yata ta kaina ta rasu.”

Soja Blessing ta rasu tana da shekaru 23, kuma za’a binne ta ranar Juma’a 27 ga watan Janairu a garin Adoka dake jihar Binuwe.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel