Yaushe Dujjal zai bayyana?

Yaushe Dujjal zai bayyana?

Ya tabbata dai a hadisai na Manzon Allah SAW cewa Dujjal zai bayyana a can karshen Duniya. Ko wanene Dujjal? Yaushe zai zo? Ya za ayi da shi?

Yaushe Dujjal zai bayyana?
Yaushe Dujjal zai bayyana?

Dujjal dai zai zo a karshen Duniya ya kuma kawo fitina babba kamar yadda Annabi SAW yayi bayani. Dujjal zai do ido guda yayin da dayan yake kuma a shafe, sannan a gaban goshin sa an rubuta ‘kafir’ da larabci. Haka Dujjal zai keta Duniya cikin ‘yan kwanaki kadan.

Dujjal dai zai rika tafiya da Jama’a wadanda suka yi imani da shi, wadanda suka kafirce masa kuma yayi masu barazanar azaba. Kai har dai na kabari bai tsira ba daga wannan mugun halitta. Saboda haka ne Manzon Allah yayi umarni da haddace da karanta Suratul Kahfi a cikin Al-Qur’ani.

KU KARANTA: Shugaban kasar Jamus ta kare Musulunci

Dujjal dai yana daga cikin alamomin karshe na tashin kiyama, tare da Mahadi da kuma Annabi Isa wanda zai dawo nan gaba kamar yadda Hadisai suka nuna. Zai zagaye Duniya kaf ban da kasar Makka mai tsarki.

Wata rana ne dai Annabi Isa AS bayan ya dawo Duniya zai isa wani wuri tare da sauran Musulmai sai ya iske Dujjal a wani Gari mai suna Lud kusa da Garin Tel-Aviv sai ya jefa masa mashi ya kashe sa.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Allah yayi mana gab-da-katar daga sharrin Dujjal. Ameen.

Asali: Legit.ng

Online view pixel