An koro yan Najeriya 253 daga kasar Libya (Dalili)

An koro yan Najeriya 253 daga kasar Libya (Dalili)

- Akalla ‘Yan Nijeriya 253 aka fatattako daga kasar libya a jiya talata 25 ga watan Afrilu

- Tarin wadannan ‘yan Nijeriyan na hade da yara 11 da manya 242 wadanda aka sauke su a filin jirgin saman dake jihar Legas daga jirgin kasar Libya

- An sauke su ne da misalin karfe 8:10 na daren jiya Talata

Akalla ‘Yan Nijeriya 253 aka fatattako daga kasar libya a jiya talata 25 ga watan Afrilu.

Tarin wadannan ‘yan Nijeriyan na hade da yara 11 da manya 242 wadanda aka sauke su a filin jirgin saman Murtala Muhammad International Airport dake jihar Legas daga jirgin kasar Libya mai suna ‘Libyan Airline’ a misalin karfe 8:10 na daren jiya talata.

Legit.ng ta samu labarin cewa Darakta Janar na hukumar kula da ayyukan gaggawa NEMA, Injiniya Mustapha Maihaja ya labarta cewa za a baiwa wadannan yan Nijeriyan da aka fatattako guzurin kudin motan komawa zuwa yankunasu da kauyukansu.

An koro yan Najeriya 253 daga kasar Libya (Dalili)
An koro yan Najeriya 253 daga kasar Libya (Dalili)

KU KARANTA: An kama wani kato yana lalata da yaro dan shekara 12

Kamata ya yi a sanar da wadannan matafiya masu zuwa neman kudi kasasshen wajen Nijeriya da cewa, za su iya samun fiye da abin da suka je nema kasasshen waje a Nijeriya, in har suka yi hakuri da zama a kasarsu, Nijeriyar yanzu ba irin ta da bace, abubuwan suna canjawa kuma za a samu cigaba in aka yi hakuri, inji daraktan

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Yan Najeriya a filin jirgin sama

Asali: Legit.ng

Online view pixel