Hukumar INEC ta tsai da ranar sake zabe a jihar Katsina

Hukumar INEC ta tsai da ranar sake zabe a jihar Katsina

- Hukumar zabe ta shiyar Katsina ta ce ta tsai da ranar 20 ga watan Mayu a matsayin ranar sake zaben mazabar Mashi / Dutsi ta tarayya

- Kura ya ce jam'iyyun siyasa za su gudanar da zaben fitar da dan takara tsakanin watan Mayu 1 zuwa 4, 2017

- Kura ya tabbatar da cewa za a fara gangamin kamfen daga watan Mayu 5 da kuma kawo karshe a ranar 19 na watan

Hukumar zabe mai zaman kansa (INEC) ta tsai da ranar 20 ga watan Mayu a matsayin ranar sake zaben mazabar Mashi / Dutsi ta tarayya a Jihar Katsina.

Legit.ng ta ruwaito cewa za a yi wannan zaben cika gurubin mazabar ne sanadiyar rasuwar dan majalisar mai wakiltar mazabar, Alhaji Sani Bello a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2017.

Jami’in hukumar, Mista Yunusa Kura ya bayyana haka a ranar Laraba, 26 ga watan Afrilu a Katsina a lokacin wata taron ruwa da tsaki a jihar.

KU KARANTA KUMA: Har yanzu babu kasafin kudin wannan shekarar a Najeriya

Kura ya ce a na sa ran jam'iyyun siyasa za su gudanar da zaben fitar da dan takara tsakanin watan Mayu 1 zuwa 4, 2017.

Ya ce jam'iyyun siyasa za su fara gangamin kamfen daga watan Mayu 5 da kuma kawo karshe a ranar 19 na watan.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Yadda hukumar EFCC ta gurfanar da wasu jami'in hukumar zaben na INEC a kotu a cikin wannan bidiyo

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel