Yadda Inyamurin Najeriya ya auri Musulma yar kasar Malaysia

Yadda Inyamurin Najeriya ya auri Musulma yar kasar Malaysia

- Wani Inyamuri dan Najeriya yayi gwaninta inda ya auro mata musulma yar kasar Malaysia

- Yan uwan amaryar da abokan ango duk sun halarci taron daurin auren

Soyayya ruwan zuma, kamar yadda Hausawa ke fadi, kuma dama ai matar mutum kabarinsa, kamar haka ne wani rahoto da Legit.ng ta samu dake nuna tsananin soyayyar data shiga tsakanin wasu masoya biyu mabiya addinai daban daban kuma yan kasa da kabila daban daban.

Wasu hotunan dake ta yawo a shafukan kafafen sadarwa sun nuna yadda wani dan Najeriya daga kabilar Inyamurai ya auri wata kyakkyawar yarinya musulma 'yar kasar Malaysia.

KU KARANTA: Buratai ya jagoranci bikin ƙaddamar da sansanin sojoji a Daura

Wannan Inyamuri mai suna Collins, ya auri budurwar tasa ne a ranar Asabar 20 ga watan Mayu, inda aka daura auren nasu a gundumar Jasin dake garin Melaka a kasar ta Malesiya.

Yadda Inyamurin Najeriya ya auri Musulma yar kasar Malaysia
Yayin daurin auren Collins da amaryarsa

A cikin hotunan an hangi yan uwan amaryar Collinsa tare da yan’uwa da abokan angon duk sun halarci taron daurin auren.

Yadda Inyamurin Najeriya ya auri Musulma yar kasar Malaysia
Ango da Amarya

Mu a anan sai dai muce Allah ya bada zaman lafiya.

Ga sauran hotunan nan:

Yadda Inyamurin Najeriya ya auri Musulma yar kasar Malaysia
Yan uwa da abokan arziki

Yadda Inyamurin Najeriya ya auri Musulma yar kasar Malaysia
Mahalarta auren

Yadda Inyamurin Najeriya ya auri Musulma yar kasar Malaysia
Abokan ango

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Yan mata sun bayyana nawa suke son namiji su ya mallaka kafin su aure shi

Asali: Legit.ng

Online view pixel