Ana neman ‘Dan Marigayi Shugaba Gaddafi na Kasar Libiya ruwa a jallo

Ana neman ‘Dan Marigayi Shugaba Gaddafi na Kasar Libiya ruwa a jallo

– Babban Kotun Duniya na ICC na neman iyalin Shugaba Gaddafi

– Ana zargin shi Saif-al-Islam din da wasu laifuffuka

– Shekaru kusan 6 kenan da aka kashe Shugaba Muammar Gaddafi

Kotun Duniya na neman wani ‘Dan Marigayi Muammar Gaddafi. Kama shi dai zai iya kara kawo rikici a Yankin na Libiya. Kuma dai har yanzu ba a san inda ‘Dan tsohon shugaban yake ba.

'Dan Marigayi Shugaba Gaddafi na Kasar Libiya
‘Dan Marigayi Shugaba Gaddafi na Libiya

Cikin ‘yan kwanakin nan ne aka saki ‘Dan Marigayi Shugaba Muammar Gaddafi na kasar Libiya a karkashin wani lamuni. Sai dai babban Kotun Duniya ICC na neman sa kuma ruwa a jallo cewa ya aikata wasu laifuffuka lokacin Mahaifin sa na mulki.

KU KARANTA: Abin tausayi: Karanta labarin wani Dan Kano da ke Legas

Ana neman ‘Dan Marigayi Shugaba Gaddafi na Kasar Libiya ruwa a jallo
Saif-al-Islam dan gidan Marigayi Shugaba Gaddafi

Wasu dai sun soki sakin na shi da aka yi wanda har yanzu ba a san ma inda ya shige ba. ICC ke cewa dole Gwamnatin kasar ta kama shi domin a hukunta sa amma dai wasu na ganin sake sa ne zai kawo zaman lafiya a Yankin musamman yadda ya ke da magoya.

Kun ji cewa Dan Attajirar na Misis Alakija watau Folarin Alakija ya kashe kusan Biliyan 2 wajen bikin aure. Folarin ya auro wata ‘Yar kasar Iran ce da ke zaune a Ingila mai suna Nazanin Jafarian Ghaissarifar.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

An yaye wasu Sojojin saman Najeriya

Asali: Legit.ng

Online view pixel