WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE a ranar Laraba

WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE a ranar Laraba

- WAEC ta ce zata saki sakamakon WASSCE na 2017 a ranar Laraba mai zuwa

- Hukumar ta bayyana cewa nan da ranar Laraba za ta saki sakamakon WASSCE na 2017

- Hukumar tace ta kirkiro 'Project 60' don inganta sashen ilimi

WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE na 2017 a ranar Laraba mai zuwa, 19 ga watan Yuli ko kafin ranar.

WAEC ta wallafa hakan ne a shafinta ta Facebook inda ta bayyana cewa nan da ranar Laraba za ta saki sakamakon.

Hukumar ta ce sake sakamakon jarrabawar a cikin gajerar lokacin wani bangare ne na WAEC ta sabon dabarun wanda aka sani da'Project 60'.

WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE a ranar Laraba
Ofishin WAEC

Hukumar tace ta kirkiro 'Project 60' don inganta sashen ilimi.

KU KARANTA: An gano wasu azuzuwan ƙasa a Zamfara inda ɗalibai ke ɗaukan darasi (HOTUNA)

Legit.ng ta ruwaito a watannin baya cewa an yi zaman jarrabawar a ranar Litinin, 27 ga watan Maris kuma ƙare a ranar 3 ga watan Mayu 2017.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel