Biyafara: Wata Matashiya ‘yar Najeriya ta samu takadar kudin Biyafara a akwatin kakanta (Hotuna)

Biyafara: Wata Matashiya ‘yar Najeriya ta samu takadar kudin Biyafara a akwatin kakanta (Hotuna)

- Wata matashiya ta ce ta gano wasu takadar kudaden Biyafara a cikin wani akwatin kakanta

- Matashiya ta wallafa kudin ne a shafinta ta Facebook, yayin da ta ce tana alfari da kudin

- Nmesoma ta ce yanzu bakin alkalami ta bushe a kan kafa yankin Biyafara

Wata matashiya ‘yar Najeriya kuma memba na kungiyar 'yan asalin kafa yankin Biyafara (IPOB) ta samu wasu kofi na takadar kudin mutanen yankin Biyafara a cikin wani akwatin kakanta.

Matashiyar wanda aka gano a matsayin Nmesoma James, ta wallafa hotuna wasu takadar kudin ne a shafinta na Facebook yayin da ta ce ta samu kudadden ne daga cikin wasu kayyakin kakanta.

Legit.ng ta tattaro cewa, Nmesoma wanda ta kira kanta a matsayin 'Ada Biyafara', ta nuna kudin Biyafara ga magoya bayanta yayin da kuma ta ke gaskata cewa ta na alfahari da yankin Biyafara.

Biyafara: Wata Matashiya ‘yar Najeriya ta samu takadar kudin Biyafara a akwatin kakanta (Hotuna)
Nmesoma wanda ta kira kanta a matsayin 'Ada Biyafara', ta na rike da kudin Biyafara

KU KARANTA: 'Ka tsare Kanu, domin ya saba ka'idar belin sa', Matasan Arewa suka fada ma Osibanjo

Kamar yadda Nmesoma James ta rubuta:

" Shaka babu za a kafa yankin Biyafara. Babu ruwan mu da maganganun mutane. Yanzu haka na gano wannan tsabar kudin Biyafara a cikin wata akwatin kakanmu,duk kudin mutanen Biyafara ne zalla”.

Biyafara: Wata Matashiya ‘yar Najeriya ta samu takadar kudin Biyafara a akwatin kakanta (Hotuna)
Takadar kudin 'yan Biyafara

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel