Gawar marigayiya ɗiyar Sule Lamido ta iso Najeriya (Hotuna)

Gawar marigayiya ɗiyar Sule Lamido ta iso Najeriya (Hotuna)

- Gawar yarinyar Sule Lamido, Hadiza Sule Lamido ta iso Najeriya

- Hadiza ta rasu ne a wani asibitin kasar India a ranar 29 ga watann Yuli

Da yammacin ranar Laraba 2 ga watan Agusta ne gawar yarinyar tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido tai so filin sauka da tashin jirage na garin Dutse, da misalin karfe 6:27.

Wakilin jaridar Rariya ya ruwaito an hangi keyar manyan mukarraban tsohon gwamna Alhaji Sule Lamido a yayin tarbar gawar, wadanda suka hada da Alhaji Umaru, Malam Isah Duniya, Nasiru Roni, Aminu Ringim, Salisu Mamuda, Aminu Jahun, Rabiu Taura, Muhammad Habib Barded a ire irensu.

KU KARANTA: Jami’an Yansanda na neman wani ‘Malami’ wur-jan-jan sanadin abin daya aikata ma wata gawat (Karanta)

Legit.ng ta ruwaito Hadiza Sule Lamido mai shekaru 38 ta rasu ne bayan tayi jinya a wani asibiti dake kasar Indiya a ranar 29 ga watan Yulin data gabata.

Gawar marigayiya ɗiyar Sule Lamido ta iso Najeriya (Hotuna)
Gawar marigayiya

Sa’annan ta rasu ta bar mijinta, yaya uku da iyayenta. Tun bayan rasuwarta ne tsohon gwamnan keta samun gaisuwar ta’aziyya tare da jajantawa daga jama’a ciki da wajen kasar nan.

Gawar marigayiya ɗiyar Sule Lamido ta iso Najeriya (Hotuna)
Mijinta

Gawar marigayiya ɗiyar Sule Lamido ta iso Najeriya (Hotuna)
Gawar marigayiya

Gawar marigayiya ɗiyar Sule Lamido ta iso Najeriya (Hotuna)
Yan Uwa da abokan arziki

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Dalilin dayasa farashin kayan abinci ke tashi:

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel