Wike ya bayyana yadda APC za ta murde zaben 2019

Wike ya bayyana yadda APC za ta murde zaben 2019

-Sun mana alkawarin canji amma bamu ga komai ba

-Sun kara wa yansadan da ake zargin su da murde zabe mukami

-Dimokradiyya ta mutu a Najeriya

Gwamnan jihar Rivas, Nyesom Wike yace jam’iyyar All Progress Congress (APC) sun fara shirye-shiryen murde zaben 2019 ta kara wa yan sandan da ake tuhuma da laifin murde zabe mukami

Wike ya fada haka ne a wani taron lauyoyi a ranar Litinin a birnin Fatakol.

Gwamnan yace hukumar yansanda sun kara wa Mista Akin Fakorede mukami, yanzu shine kwamandan Special Anti-Robbery Squad(SARS) na jihar Rivas, mutumin da aka dauke shi a wani bidiyo yana dukan wani ma’aikacin zabe na INEC.

Wike ya bayyana yadda APC za ta murde zaben 2019
Wike ya bayyana yadda APC za ta murde zaben 2019

Wike yace: “Rundunar yan sanda sun kara ma Steve Hasso mukami zuwa assistan commissioner, saboda kokarin da yayi musu na murde zaben 10 ga watan Disamba 2016."

KU KARANTA:Anambra: Ka fara shirin mika mulki - Oyegun ya gaya ma Obiano

“Sun ma yan Najriya alkawarin canji, amma ba mu ga komai ba.

“Dimokradiyya ya mutu a Najeriya. Zuwa 2019 mutane zasu daina maganan dimokradiyya. Sun kara ma Mista Akin Fakorede mukami da ya murde zabe, Mista Stephen Hasso shima gwani ne a murde zabe. Duka sun turo su jihar Rivas ne dan su murde zaben 2019,” Inji Wike.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Bidiyo game da labaran wannan mako

Asali: Legit.ng

Online view pixel