Allah ya yi wa dan Salihu Sagir Takai rasuwa

Allah ya yi wa dan Salihu Sagir Takai rasuwa

Allah ya yi wa wani dan bautar kasa, Ibrahim Salihu Sagir Takai rasuwa a yammacin jiya Lahadi, 20 ga watan Agusta a jihar Kano.

Baá sanar da abunda ya haddasa mutuwar tasa ba amma an sanar da mutuwarsa ta shafin Facebbok.

Za’a yi jana'izar sa a yau Litinin, 21 ga watan Agusta a gidan Malam Salihu Sagir Takai dake Hadejia Road (daura da Buhari Shoping Complex Kano.

Allah ya gafarta masa Allah ya sa aljanna makoma.

Allah ya yi ma dan Salihu Sagir Takai rasuwa
Allah ya yi ma dan Salihu Sagir Takai rasuwa

Abokansa sun nuna alhini da jimami na wannan babban rashi da sukayi.

KU KARANTA KUMA: Wani mutumi ya zuba Mirinda a kasa ya sha don murnar dawowar Buhari (hoto)

Daya daga cikin abokansa mai suna Abba Mansur ya buga hotonsa tare da marigayin a shafinsa na Faceboo hade da sakon ta'aziyya.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel