N'Golo Kante ya bada dalilin shiga Chelsea

N'Golo Kante ya bada dalilin shiga Chelsea

– N’Golo Kante yace Antonio Conte ya jawo shi shiga Chelsea

-Bafaranshen yana gode ma magoya baya da karamta shi

-Kante shine na biyu da shiga Blues bayan Michy Batshuayi

An dai sayi dan wasan mai shekara 25 daga wajen zakkarun kwallo na Leicester a kan kudi £32miliyan, abin da ba'a taba ganin irinsa ba.

N'Golo Kante ya bada dalilin shiga Chelsea
N'Golo Kante

Ya ci gaba da cewa "gawurtaccen klub ne, wanda ya dauki gawurtaccen koci, yana kuma da kishin ci gaba irin wanda na ke so. Abin da klub din ya sa gaba, da maganar da kocin yayi suka sa nace da ni za'a yi wannan gagarumar abu mai dadi".

KU KARANTA : Kocin Chelsea Antonio Conte ya yaba ma N’golo Kante

Asali: Legit.ng

Online view pixel